in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana adawa da matakin Amurka na sayarwa yankin Taiwan makamai
2018-09-25 21:14:43 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya bayyana rashin amincewarsa kasar da kakkausar murya, kan kudurin Amurka na sayarwa yankin Taiwan makamai da darajarsu ta kai dala miliyan 330, sannan ta gabatar da kokenta ga bangaren Amurka kan wannan mataki.

Jami'in wanda ya sanar da hakan yayin taron maname labarai yau Talata a nan birnin Beijing, ya ce, shirin Amurka na sayarwa yakin na Taiwan makamai ya sabawa muradun dokoki da alakar kasa da kasa, da ma manufar kasar Sin daya tak a duniya da sanarwar guda uku da Sin da Amurka suka sanyawa hannu. Kuma wannan yana iya yiwa muradun tsaro da 'yancin kasar Sin illa nesa ba kusa ba.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China