in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi maraba da shawarar WHA na rashin sanya yankin Taiwan a matsayin mai sa-ido
2018-05-22 19:34:38 cri
Mahakuntan kasar Sin sun yi maraba da shawarar majalisar harkokin kiwon lafiya ta duniya(WHA) na rashin amsa bukatar yankin Taiwan na halartar taron majalisar a matsayin mai-sa-ido.

Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang wanda ya bayyana hakan yau yayin taron maname labarai, ya ce matakin da majalisar WHA ta dauka ya dada kare martaba da kimar kudurorin babban taron MDD da ma na majalisar harkokin kiwon lafiya, kuma hakan ya nuna cewa, duniya ta amince da manufar kasar Sin daya tak a duniya kuma ya yi daidai da yanayin da ake ciki a halin yanzu.

Jami'in na kasar Sin ya kara da cewa, gwamnatin kasar Sin za ta nazarci batun halartar yankin na Taiwan cikin harkokin kasa da kasa bisa manufar kasar Sin daya tak a duniya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China