in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin kabilun kasar Libyan sun bukaci gwamnati ta kakkabe makamai 'yan tawaye
2018-09-16 15:58:21 cri
Kungiyar tuntubar ta shugabanin kabilun kasar Libya, dake birnin Tarhuna, mai tazara kilomita 80 daga Tripoli babban birnin kasar, a jiya Asabar ta bukaci gwamnati data raba dukkan mayaka da makamansu a Tripoli cikin kwanaki uku.

A wata sanarwar hadin gwiwa ta shugabannin kabilun kimanin 1,800 na Libya sun ce, kabilun kasar sun shiga cikin damuwa game da halin da ake ciki, bayan tashin hankalin da ya barke, wanda ya jefa 'yayansu cikin matsanancin hali, da rasa hakkokinsu, da kwace musu duk wata damar siyasa da suke da ita sakamakon yadda mayakan suka kwace dukkan madafun iko da duk wani ikon fada a ji a kasar.

Sanarwar ta kuma bukaci mayakan a babban birnin kasar Tripoli da su mika makamansu kuma a rusa dukkan hukumomin gudanarwar kungiyoyin mayakan bayan an raba su da makamansu.

A 'yan kwanakin da suka gabata ana fuskantar karuwar tashin hankali tsakanin dakarun gwamnati da mayakan runduna ta 7 daga Tarhuna, lamarin da ya yi sanadiyyar rayukan mutane 78 da kuma jikkata wasu 210. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China