in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Libya ta ayyana dokar ta baci a Tripoli
2018-09-04 13:56:57 cri
Gwamnatin Libya dake samun goyon bayan MDD ta ayyana dokar ta baci a Tripoli, babban birnin kasar sakamakon tashin hankali da fadan da ya barke tun a ranar Litinin din da ta gabata tsakanin dakarun gwamnati da mayaka masu dauke da makamai

Wata sanarwar da mahukuntan kasar suka fitar ta bayyana cewa, sakamakon kazantar da al'amura ya sa majalisar zartarwar gwamnatin hadaka ta ayyana dokar ta baci ta gaggawa a Tripoli, babban birnin kasar da nufin kare rayukan fararen hula da dukiyoyin gwamnati da na sassa masu zaman kansu.

Sanarwar ta kara da cewa, gwamnati ba za ta lamunci yadda ake karya dokoki da matakan tsaro a birnin na Tripoli ba, don haka yanayin na bukatar daukar dukkan matakan tsaro da na soja gami da na fararen hula da suka wajaba.

Rahotanni na cewa, tun a ranar Litinin din da ta gabata, kudancin birnin Triploli ke fuskantar tashin hankali tsakanin gwamnati da dakaru masu dauke da makamai, lamarin da ya kai ga mutuwar mutane 41 kana wasu 123 kuma suka jikkata. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China