in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Libya ta yaba da takunkumin da kwamitin sulhun MDD ya kakabawa jagoran 'yan tawaye
2018-09-13 13:56:21 cri
Gwamnatin kasar Libya ta jinjinawa kwamitin sulhun MDD, bisa takunkumin da ya kakabawa jagoran 'yan tawayen kasar Ibrahim Jathran, bayan da aka zargi kungiyar sa da kaddamar da hari kan kamfanin man fetur na kasar NOC.

A ranar Talata, kwamitin sulhun MDDr ya yanke shawarar kakabawa Jathran takunkumin hana tafiye tafiye, da daskaras da kadarori. Kafin hakan, babban mai shari'ar kasar ta Libiya, ya fitar da sammacen cafke jagoran na 'yan tawaye bayan aukuwar wani harin na daban, a sansanin dake kunshe da ma'adanar mai mafi girma a kasar, wadda ke da nisan kilomita 500 daga gabashin birnin Tripoli fadar mulkin kasar.

Harin na baya, wanda kungiyar Jathran ta kaddamar ya auku ne a watan Yunin da ya shude, lokacin da dakarun ta suka kai farmaki a yankin, suka kuma kwace kusan rabin sa, kafin daga bisani dakarun gwamnatin kasar tsagin gabashi su fatattake su, a wata arangama da ta yi sanadiyyar kisan sojoji 34. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China