in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka mutu a rikicin Tripoli ya kai 78
2018-09-10 13:05:49 cri
Ma'aikatar lafiyar kasar Libya ta sanar da cewa adadin mutanen da suka mutu a sanadin tashin hankalin da ya barke tsakanin dakarun gwamnati da mayakan 'yan tada kayar baya a Tripoli babban birnin ksar Libya ya kai 78.

Sashen kula da masu fama da raunuka na ma'aikatar lafiyar kasar ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, tashin hankalin Tripoli yayi sanadiyyar rayuka 78 da kuma jikkata mutane 210.

Sanarwar tace kawo yanzu an riga an sallami mutane 103 daga asibiti bayan an duba lafiyarsu, kana wasu mutanen 16 sun bace.

A baya bayan nan birnin Tripoli yana fuskantar tashin hankalin wanda ya kaure tsakanin sojojin gwamnati da mayaka runduna ta 7 a kusa da birnin Tarhuna, mai tazarar kilomita 80 a kudu maso gabashin Tripoli.

A ranar Alhamis, ofishin MDD dake Libya ya sanar da cewa bangarorin da basa ga maciji da juna sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsagaita bude wuta da nufin kawo karshen tashin hankalin da ya barke, wanda yayi sanadiyyar raba magidanta 1,800 da matsugunansu.

Tun bayan tashin hankalin da ya barke a shekarar 2011 wanda yayi sanadiyyar kifar da gwamnatin tsohon shugaban kasar Muammar Gaddafi, Libya take cigaba da fuskantar tashe tashen hankula, da rudanin siyasa da rarrabuwar kawuna a tsakanin jama'ar kasar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China