A halin yanzu matsalar rashawa ta zama ruwan dare a tsakanin dukkan kasashen duniya, masu arziki da matalautan kasashe, arewaci da kudanci, wadanda suka cigaba da masu tasowa, ya tabbatar da hakan ne ga kwamitin sulhu MDDr.
Ya ce wajibi ne mambobin kasashen duniya su tashi tsaye wajen yakar rashawa. Ya kara da cewa, abu ne mai matukar muhimmanci kasashe su kafa wani tsari na baiwa hukumomin yaki da rashawa kwarin gwiwa wajen hukunta dukkan laifukan dake da nasaba da rashawa.
Dandalin tattalin arziki na kasa da kasa yayi kiyasin ana tafka hasarar a kalla dalar Amurka trillion 2.6 ko kuma kashi 5 bisa 100 na GDP na kasashen duniya a sanadiyyar ayyukan rashawa.
A cewar bankin duniya, 'yan kasuwa da daidaikun mutane suna biyan dala biliyan 1 a duk shekara a matsayin cin hanci. (Ahmad Fagam)