in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya: An nada sabon jagoran hukumar tsaro ta farin kaya
2018-09-14 09:27:45 cri
Shugaba Muhammadu Buhari na tarayyar Najeriya, ya nada Yusuf Magaji Bichi, a matsayin sabon shugaban hukumar tsaro ta farin kaya DSS. Wata sanarwa da fadar shugaban kasar ta fitar, ta bayyana sabon shugaban hukumar ta DSS a matsayin kwararre, wanda ya goge a fannin aikin sa. Zai kuma fara wa'adin aikin sa a Juma'ar nan.

Sanarwar ta kara da cewa, Yusuf Magaji Bichi ya yi aiki a sassan hukumar DSS daban daban, ya kuma rike mukamai a fannonin tattara bayanan sirri, da na gudanar da bincike, da warware rikici, da kaucewa fadawa hadurra, da na yaki da ta'addanci, da na ba da kariya, da kuma na kula da ma'aikata. Kafin nadin na sa, ya rike mukamin daraktan hukumar a wasu jahohin Najeriya.

A ranar 7 ga watan Agusta ne gwamnatin Najeriya ta sauke Lawal Musa Daura daga mukamin shugabancin hukumar ta DSS, sakamakon zargin sa da aka yi da tura jami'an hukumarsa zuwa harabar majalissar dokokin kasar, inda suka kewaye majalissar tare da hana 'yan majalissar shiga. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China