in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani wani abu ya fashe a wani gidan mai a Najeriya
2018-09-11 20:52:49 cri
Yau Talata, rundunar 'yan sandan Najeriya ta tabbatar da cewa, gobara ta tashi a wani gidan mai dake birnin Lafia na jihar Nassarawa dake tsakiyar kasar jiya Litinin, abun da ya yi ajalin mutane a kalla 35 tare da jikkatar wasu sama da dari.

Hukumar bada agajin gaggawa reshen jihar Nassarawa ta fitar da wata sanarwa tana mai cewa, hadarin ya faru ne sakamakon yoyon man fetur, kana ta ce, galibin wadanda suka mutu mutane ne da suka zo kashe kwarkwatan ido. Bayan da wutar ta watsu zuwa babbar hanyar mota da ta nufi Abuja, fadar mulkin kasar, akwai motoci da babura da dama wadanda suka kone su kurmus.

A yau ne kuma, shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya fitar da wata sanarwa, inda ya nuna damuwa sosai kan babbar hasarar da aka yi, ya kuma yi kira ga mahukuntar wurin da su tabbatar da samar da duk wata kulawa da ta kamata ga mutanen da suka ji rauni.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China