in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Zimbabwe ya bukaci Amurka da ta nuna adalci game da yanayin da ake ciki a Zimbabwe
2018-08-16 19:21:26 cri
Shugaba Emmerson Mnangagwa na Zimbabwe ya bukaci kasar Amurka da ta fahimci zahirin yanayin siyasar kasar da ake ciki.

Kalaman shugaban na zuwa ne, baya da jaridar Herald da ake wallafa a kasar ta buda wani rahoto a jiya cewa, shugaba Mnangagwa ya shaidawa manema labarai bayan ganawa da sabon jakadan Amurka dake kasar ta Zimbabwe Brian Nicholas ranar Laraba cewa, ya kamata sabon jakadan da ya kama aiki a watan Yulin wannan shekara ya fahimci abin da ke faruwa a kasar.

Jakada Nicholas ya ziyarci Mnangagwa ne 'yan kwanaki bayan shugaba Donald Trump na Amurka ya sake kakabawa kasar takunkumi. Ya kuma bukaci kotun kundin tsarin mulkin kasar Zimbabwen da nuna gaskiya yayin da take sauraron korafin sakamakon zaben da jagoran 'yan adawar kasar na jam'iyyar MDC Nelson Chamisa ya gabatar mata.

Chamisa dai yana kalubalantar nasarar kaso 50.8 cikin 100 da aka ce Mnangagwa ya samu a zaben shugaban kasar da ya gudana, yayin da shi kuma ya samu kaso 44.3 cikin 100 na kuru'un da aka kada.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China