in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin zai halarci taron dandalin tattauna tattalin arzikin gabashin kasashen duniya
2018-09-11 11:13:07 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya bar Beijing a yau Talata, domin halartar taron dandalin tattauna tattalin arziki na gabashin kasashen duniya karo na 4 da zai gudana a birnin Vladivostok na Rasha, bisa gayyatar da takwaransa na Rashar Vladimir Putin ya yi masa.

'Yan rakiyar Shugaba Xi sun hada da Ding Xuexiang, mamba a ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na JKS, kuma mamba a sakatariyar kwamitin tsakiya na jam'iyyar da Darakta Janar na ofishin kwamitin tsakiya na JKS Yang Jiechi, da mamba a ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na JKS kuma mamba a majalisar gudanarwar kasar, kana Ministan harkokin waje wato Wang Yi, da kuma mataimakin shugaban kwamitin majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa na al'ummar kasar Sin kuma shugaban hukumar rayawa da sake fasalin kasar wato He Lifeng. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China