in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi ya bukaci a rika girmama malamai da harkar ilimi
2018-09-10 14:49:11 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira ga JKS da daukacin al'ummar kasar, da su inganta dabi'ar girmama malamai da harkar ilimi.

Shugaba Xi wanda kuma shi ne Sakatare Janar na kwamitin tsakiya na JKS kuma shugaban rundunar sojin kasar, ya bayyana haka ne yayin wani taron kasa da ya gudana yau Litinin domin ranar Malamai ta kasar Sin karo na 34.

Ya ce a madadin kwamitin tsakiya na jam'iyyar, ya na mika sakon gaisuwa da taya murna ga malamai a fadin kasar.

Ya kuma jadadda bukatar daukaka kwarewa da darajar malamai ta yadda za su mori matsayinsu a cikin al'umma da kuma kara bada gudunmuwa ga maradun jam'iyyar da jama'a, ta hanyar ilmantar da su. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China