in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya taya murnar cika shekaru 70 da kafuwar kasar Koriya ta Arewa
2018-09-09 16:55:11 cri
Babban sakataren kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin kuma shugaban kasar Xi Jinping ya aika sako ga shugaban jam'iyyar WPK kuma shugaban kwamitin gudanarwar kasar Koriya ta Arewa Kim Jong Un don taya shi murnar cika shekaru 70 da kafuwar kasar Koriya ta Arewa a ranar 9 ga wannan wata.

A sakonsa, Xi Jinping ya bayyana cewa, a cikin shekaru 70 da kafuwar kasar Koriya ta Arewa, jama'ar kasar sun samu nasarori da dama kan sha'anin raya ra'ayin gurguzu da raya kasa.

Xi Jinping ya jaddada cewa, jam'iyyar kwaminis ta Sin da gwamnatin kasar Sin suna dora muhimmanci sosai kan dangantakar hadin gwiwa da sada zumunta a tsakaninta da kasar Koriya ta Arewa, Sin ta tsaya tsayin daka kan manufar kiyayewa da zurfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. A shekarar bana, shugaba Xi ya gana da Kim Jong Un har sau karo uku, sun tabbatar da makomar raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. Shugaba Xi yana son yin kokari tare da Kim Jong Un wajen sa kaimi ga raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu yadda ya kamata don amfanawa kasashen biyu da jama'arsu gaba daya da kuma samun zaman lafiya da na karko a yankin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China