in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashe 42 suka rattaba hannu kan yarjejeniyar inganta ayyukan zaman lafiya ta MDD
2018-09-11 10:23:25 cri
Jimilar kasashe 42 ne suka rattaba hannu kan yarjejeniyar inganta ayyukan wanzar da zaman lafiya ta MDD, a wani bangare na yunkurin Sakatare Janar na Majalisar, na sake sabunta goyon bayan da MDD ke ba ayyukan wanzar da zaman lafiya.

Kakakin majalisar Stephane Dujarric, ya ce kasashe 42, ciki har da wadanda suka fi ba majalisaar gudunmowar 'yan sanda da sojoji, da mambobin kwamitin sulhu ne suka amince da yarjejeniyar aiki tare na taimakawa ayyukan wanzar da zaman lafiya na majalisar.

Ya kuma godewa dukkan kasashen da suka sanya hannu kan daftarin, yana mai cewa, Sakatare Janar Antonio Guterres, na kira ga dukkan mambobin mjalisar, su rattaba hannu kan daftarin kafin ranar 14 ga watan Satumba, gabanin taron manyan jami'ai kan tsarin ayyukan wanzar da zaman lafiya da za a yi ranar 25 ga watan na Satumba.

Taron zai bayyana rawar da MDD ta taka a baya, da kuma wadda take yi a yanzu ga ayyukan wanzar da zaman lafiya da bayyana kalubalen da take fuskanta da kuma taimakawa wajen inganta shigar sauran kasashen duniya cikin aikin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China