Cikin wata sanarwa da sashen ya fitar a jiya Litinin, ya bayyana rashin gamsuwa da yadda ofishin kungiyar ta PLO ya gaza, wajen gudanar da ayyukan sa yadda ya kamata.
To sai dai kuma a nasu bangaren, jami'an ofishin na PLO, wadanda tuni aka sanar da su kudurin na gwamnatin shugaba Trump, sun yi watsi da zargin na Amurka, suna masu cewa matakin nuna karfin tuwo ne kawai, da kuma yanke hukunci ba tare da yin cikakken nazari ba. (Saminu Alhassan)