in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Angola ya zama shugaban jam'iyya mai mulkin kasar
2018-09-09 16:21:31 cri
Bisa labarin da kamfanin dillancin labaru na kasar Angola ya bayar, an ce, jam'iyyar 'yantar da jama'ar kasar Angola wato jam'iyyar dake kan karagar mulkin kasar ta sanar a ranar 8 ga wata cewa, shugaban kasar Angola Joao Lourenco ya zama sabon shugaban jam'iyyar.

An ce, jam'iyyar 'yantar da jama'ar kasar Angola ta sanar da wannan kuduri a wajen taron musamman da aka gudanar a birnin Luanda dake kasar.

Lourenco ya gudanar da ayyukan harkokin jam'iyyar da majalisar dokokin kasar a dogon lokaci, ya zama ministan tsaron kasar tun daga shekarar 2014, kuma ya zama mataimakin shugaban jam'iyyar 'yantar da jama'ar kasar Angola tun daga watan Agusta na shekarar 2016. A ranar 26 ga watan Satumba na shekarar 2017, Lourenco ya yi rantsuwar kama aiki na shugabancin kasar ta Angola. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China