in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Angola ta shiga ciki jerin kasashen duniya masu karfin tauraron dan Adam
2018-01-04 10:37:53 cri
Jakadan Rasha a Angola Vladimir Tararov, ya ce la'akari da tauraron da Adam na Angola wato Angosat-1 dake shawagi a sararin samaniya, yanzu kasar ta shiga cikin jerin kasashe masu karfin fasahar tauraron dan Adam.

Cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai, jakadan ya tabbatar da cewa dukkan wasu bangarori na tauraron Angosat-1 na aiki kamar yadda aka tsara.

Ya kara da cewa, da Angosat-1, al'ummar kasar za su samu cin gajiyar fasahohin zamani da ake samu daga tauraron dan Adam, don samun tasoshin talabijin da karfin intanet domin samun ilimin fasahohi da kiwon lafiya daga wuri mai nisa da sauran alfanu.

Jakadan ya ce karuwar samun bayanai daga tauraron zai inganta ci gaban kasar musamman a bangaren masana'antu da harkokin banki da kuma tsaro. (Fa'iza Musatpha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China