in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya na fatan daga matsayin alakarta da Sin
2018-08-31 20:01:38 cri
Tawagar Najeriya da za su halarci taron kolin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka da zai gudana a birnin Beijing na kasar Sin za ta mayar da hankali wajen daga matsayin alakar Sin da Najeriya.

Mai magana da yawun shugaban Najeriya Malam Garba shehu wanda ya sanar da hakan Jumma'ar nan cikin wata sanarwa, ya ce shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ne zai jagoranci sama da manyan jami'an gwamnatin kasar 20 zuwa kasar Sin don halarta taron na FOCAC da zai gudana a ranar 3 da 4 ga watan Satumba.

Garba shehu ya ce, yayin ganawarsa da takwaransa na kasar Sin shugaba Buhari zai tattauna kan kudaden samar da ayyukan more rayuwa a Najeriya.

Haka kuma shugaba Buhari zai yi amfani da wannan dama wajen kimanta irin ci gaba da aka samu ya zuwa wannan lokaci kan taimakon da kasar Sin ke baiwa Najeriya a fannin samar da muhimman kayayyakin more rayuwa a kasar, musamman ayyukan gina layin dogo da samar da wutar lantarki dake gudana.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China