in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi kira da a tsagaita bude wuta a Tripoli ba tare da bata lokaci ba
2018-08-28 10:26:46 cri
Shirin wanzar da zaman lafiya na MDD dake aiki a Libya UNSMIL, ya yi kira da gaggauta tsagaita bude wuta a birnin Tripoli, wanda ke fuskantar arangama tsakanin dakarun gwamnati da 'yan tawaye, tun ranar Lahadin da ta gabata.

Shirin ya bayyana damuwa game da bude wuta kan yankunan dake da yawan al'umma, wanda ya ce barazana ce ga rayukan fararen hula, ya na mai tunatarwa bangarorin biyu hakkin dake wuyansu na kare fararen hula bisa tanadin dokokin tabbatar da 'yancin bil adama da na jin kai na duniya.

Ya kuma jadadda cewa, ba zai yuwu a cimma muradun siyasa ta hanyar rikici ba, inda ya yi gargadin cewa, karuwar 'yan tawaye da rikice-rikice na iya fadada fito na fito tsakaninsu da sojoji.

Hukumar tsaro a Tripoli, ta ce ana fama da rikici a kudancin birnin tsakanin dakarun gwamnatin kasar da MDD ke marawa baya, da 'yan tawaye, wanda kawo yanzu ya yi sanadin mutuwar farar hula guda da raunata wasu da dama.

Kawo yanzu ba a san musababbin rikicin da aka yi kwanaki ana yi a kudancin Tripoli ba. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China