in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman MDD ya yi kira da a kara kokari a kasar Libya
2018-07-17 14:02:11 cri
Manzon musamma na babban sakataren MDD dake kula da batun Libya Ghassan Salame ya ce, ko da yake an soma samun kyautatuwar fannonin siyasa da na jin kai a kasar Libya, akwai bukatar bangarori daban daban su ci gaba da kokarinsu a kasar.

Salame ya bayyana haka ne yayin da yake ba da rahoto ga kwamitin sulhu a jiya Litinin a Tripoli babban birnin kasar, game da halin da Libya ke ciki da yadda ake aiwatar da shirin matakai a Libya da MDD ta gabatar, inda ya kara da cewa, a cikin 'yan watanni na farkon bana, an kwantar da kura a kasar Libya. An kuma shirya zaben kananan hukumomi karkashin goyon bayan MDD, kana an sake kafa ofisoshin MDD a Tripoli da Banghazi, haka zalika an soma yunkurin shawarwari.

Baya ga haka, Salame ya ce, wannan wani muhimmin sashe ne na shirin wanda ya sa jama'ar Libya gaba cikin tsarin siyasar kasar, kuma wannan ne karon farko da suka sa himma wajen shiga yunkurin farfado da tsarin siyasa da shawarwari. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China