in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manufar yin gyare-gyare da bude kofa ta kasar Sin na karfafawa Afrika gwiwa
2018-08-24 15:31:37 cri
An bayyana manufar yin gyare-gyare a cikin gida da bude kofa ta kasar Sin, a matsayin abun misali ga nahiyar Afrika, game da yadda za ta aiwatar da sauye-sauye a tsarin siyasa da tattalin arziki domin ci gabanta a nan gaba.

Sheriff Ghali Ibrahim, shehun malami a sashen nazarin kimiyyar siyasa da huldar kasa da kasa a Jami'ar Abuja dake Nijeriya ne ya bayyana haka yayin da yake zantawa da kamfanin dillacin labarai na Xinhua.

Sheriff Ghali Ibrahim, ya ce kamar kowacce nahiya a duniya, Afrika na samun kwarin gwiwa daga ci gaban kasar Sin, ya na mai cewa kasar Sin na zaburar da Afrika. Ya ce kayakin more rayuwa da Sin ta gina a Afrika sun samar da ci gaban da zai kai Afrika ga wani sabon mataki.

Cikin shekaru 40 da suka gabata, kasar Sin ta samu dimbin ci gaba ta fuskar tattalin arziki da zamantakewa bisa aiwatar da manufarta ta yin gyare-gyare a cikin gida da bude kofa ga kasashen ketare.

Da hadin gwiwarta da kasar Sin, Afrika na fatan ita ma za ta samu ci gaba wata rana. Domin ta hanyar hadin gwiwarta da kasar Sin, nahiyar Afrika ta bude kofarta, musammam ta dandalin tattauna hadin gwiwar bangarorin biyu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China