in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi: Wajibi ne G20 ta kara bai wa kasashe masu tasowa zarafi da goyon baya
2018-05-22 10:11:20 cri

A jiya Litinin, bisa agogon birnin Buenos Aires, hedkwatar kasar Argentina, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya halarci zama na biyu, na taron ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar G20, inda ya yi jawabi game da kara azama kan samun adalci da ci gaba mai dorewa.

A cikin jawabinsa, Wang Yi, ya yi nuni da cewa, a matsayinta na muhimmin dandalin hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa ta fuskar tattalin arziki, an dora wa kungiyar G20 alhakin kara bai wa kasashe masu tasowa zarafi, ta hanyar sa kaimi kan ci gaban tattalin arzikin duniya, da kuma kara ba su goyon baya ta hanyar inganta hadin gwiwar duniya ta fuskar bunkasuwa.

Ministan harkokin wajen na kasar Sin, ya kara da cewa, za a ci gaba da goyon bayan bunkasar kasashen Afirka. A yayin taron koli na Hangzhou da na Hamburg, an tsai da kudurin goyon bayan raya masana'antu da kara zuba jari a kasashen Afirka da kasashe mafiya rashin ci gaba. Sannan, za a ci gaba da goyon bayan ci gaban Afirka bisa tanade-tanaden da ke cikin "ajandar kungiyar Tarayyar Afirka ta shekarar 2063" kuma bisa ka'idojin "kasashen Afirka ne suka gabatar da bukatunsu, suka kuma amince da shirin da aka gabatar musu, sa'an nan an gudanar da ayyuka masu ruwa da tsaki, karkashin shugabancin Afirka". (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China