in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bukaci Kamaru da ta magance hadurran dake faruwa a titunan kasar
2018-08-24 10:30:24 cri
Wani rahoton hadin gwiwa da hukumar raya tattalin arzikin kasashen dake gabashin Afirka(EAC) da hukumar MDD mai kula da harkokin tattalin arzikin kasashen Turai(ECE) suka fitar, ya bukaci gwamnatin kasar da ta dauki matakan da suka wajaba don rage yawan mutanen dake rasa rayukansu da jikkata sakamakon hadurran dake faruwa a kan titunan kasar.

Rahoton wanda manzon musamman na babban sakataren MDD mai kula da ayyukan kiyaye hadurra a kan tituna Jean Todt ya gabatar, ya kuma bayyana cewa daga shekarar 2011 zuwa wannan lokaci, kimanin mutane 1,500 ne suke mutuwa sanadiyar hadurran mota sama da 16,000 a kowa ce shekara a kasar ta Kamaru.

A don haka jami'in ya ce, MDD ta fatan mahukuntan Kamarun za su dauki managartan matakan da za su kai ga dakile kaso 50 cikin 100 na hadrurran dake faruwa a titunan kasar, kamar yadda ke kunshe cikin matakan rage aukuwar hadurran mota da MDD ta tsara. Ya kuma bayyana kudurin MDDr na taimakawa kokarin kasar ta Kamaru na rage aukuwar hadurra a kan titunan kasar. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China