in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Kamaru ta musanta cewa sojojinta sun harbe mutanen da ba sa dauke da makami
2018-08-17 09:43:41 cri
Ministan yada labarai kuma kakakin gwamnatin kasar Kamaru, Issa Tchiroma Bakary, ya yi watsi da wani bidiyon da ya ce shiryawa aka yi, wanda ya nuna sojojin Kamaru na kashewa tare da cin mutuncin mutane a yankin arewa mai nisa na kasar.

Bidiyon da aka fitar a ranar Juma'ar da ta gabata ya nuna yadda sojoji ke ta harbi da bindigogi kan wasu mutane dake zaune jikin bango, fuskokinsu na kallon kasa.

Yayin wani taron manema labarai da ya gudana jiya a Yaounde babban birnin kasar, Issa Bakary ya ce gwamnati ta yi tir da wannan bidiyo da ta bayyana a matsayin na rashin imani da ba za a amince da shi ba. Ya kara da cewa, yayin da ake zargin sojojin kasar, daga cikin bidiyon akwai wata murya dake cewa sojojin wata kasa ne suka aikata kisan.

Jawabin nasa na zuwa ne bayan rahoton da wata kungiyar kasa da kasa ta fitar, ta na mai cewa sojojin Kamaru ne suka aikata kisan yayin wani aiki da suka yi a kauyen Achigaya dake yankin arewa mai nisa na kasar.

Ministan ya ce sojojin Kamaru masu da'a ne da suka san aikinsu, kana suna da kyakkyawar alaka da jama'a. Sai dai kuma ya sanar da cewa ana gudanar da bincike a kai.

Har ila yau, ya ce yanzu haka, akwai hukumar dake jagorantar bincike kan lamarin domin gano wadanda ke da hannu. Ya ce idan aka gano sojojin Kamaru ne, to za a gurfanar da su gaban kotu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China