in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatar kudin Amurka ta sanar da saka takunkumi kan wasu kungiyoyi da daidaikun jama'a da ke da alaka da Rasha
2018-08-22 10:56:01 cri
Ma'aikatar kudin Amurka ta sanar a jiya Talata cewa, za a saka takunkumi ga wasu kungiyoyi da daidaikun jama'a dake da nasaba da kasar Rasha, bisa dalilin kaucewa ko sabawa takunkumin Amurka da suka yi.

Ma'aikatar ta ce, wadanda aka sanya musu takunkumin sun hada da kungiyoyi biyu da daidaikun jama'a biyu dake da alaka da kasar Rasha. Bisa dokokin da suka shafi muggan ayyukan yanar gizo na Amurka, ma'akatar ta yi zargin cewa, sun kaucewa takunkumin kasar, ta hanyar taimakawa wata kungiyar kasar Rasha, wadda ta sanyawa takunkumi. A wannan gaba kuma, Amurka ta kuma sanya takunkumi kan wasu kungiyoyi biyu da jiragen ruwa 6 dake da alaka da Rasha, sakamakon zarginsu da ake na mika tataccen mai tsakaninsu da wasu jiragen ruwa masu rataye da tutar kasar Koriya ta arewa. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China