A yayin da yake ganawa da firaminista Mohamad, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya nuna yabo matuka kan goyon bayan da Mr. Mohamad yake baiwa kasar Sin kan raya shirin "Ziri daya da hanya daya", da kuma babbar gudummawar da ya bayar wajen inganta hadin gwiwar dake tsakanin kasashen Asiya baki daya. (Maryam)