in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude sakateriyar wucin-gadi ta cibiyar hadin-gwiwar Sin da Afirka a fannin muhalli a kasar Kenya
2018-08-18 16:25:02 cri
An kaddamar da sakateriyar wucin-gadi ta cibiyar hadin-gwiwar Sin da Afirka a fannin kiyaye muhalli a Nairobin Kenya, inda wakilai daga kasar Sin da kasashen Afirka 53 gami da hukumar kiyaye muhalli ta Majalisar Dinkin Duniya suka halarci bikin. Rahotanni na cewa, wannan cibiya za ta taimaka tare da bada goyon-baya ga aiwatar da shirin kiyaye muhalli na Sin da Afirka, wadda za ta zama muhimmin dandali wajen yin shawarwari tsakanin bangarori daban-daban da kuma tattara kudade.

A watan Disamban shekarar 2015 ne aka tsaida kudurin kafa cibiyar hadin-gwiwar Sin da Afirka ta fuskar kiyaye muhalli a wajen taron kolin dandalin FOCAC a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu. Kafa irin wannan cibiya muhimmin mataki ne da aka dauka wajen tabbatar da aiwatar da wasu manyan shirye-shirye goma na inganta hadin-gwiwar Sin da Afirka. Kana, Sin za ta aiwatar da wasu ayyuka 100 na samar da makamashi mai tsabta da na neman ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba a nahiyar Afirka.

A dayan bangaren kuma, kokarin da kasar Sin take yi wajen kiyaye muhalli ya samu amincewa da yabo daga kasashen duniya. Inda mataimakiyar darektar zartaswa ta hukumar kiyaye muhalli ta MDD, Madam Joyce Msuya ta ce, kasar Sin ta yi kwaskwarima a fannin kiyaye muhalli, da son koyawa sauran kasashe nasarorin da ta samu a wannan fanni. Joyce ta ce, karfafa hadin-gwiwar Sin da Afirka a fannin muhalli zai amfanawa jama'ar Afirka baki daya.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China