"Jami'anmu suna wajen da aka yi harbe harben a kan titin Kingsbury da misalin karfe 9:45 na dare daidai karfe (2045GMT) agogon GMT a ranar Litinin. Ba shi da alaka da ta'addanci. An kwashe mutane 3 zuwa asibiti, wadanda aka yi ammana ba su da cutarwa," "yan sandan birnin London sun bayyana hakan a cikin shafinsu na Twitter.
Kakakin hukumar 'yan sandan ya ce: "'Yan sanda da motar daukar marasa lafiya na London suna zaune cikin shirin ko-ta-kwana tun da misalin karfe 9:45 a daren Litinin, 20 ga watan Augasta, tun bayan samun rahotannin harbe harben a titin Kingsbury."
'Yan sandan sun ce an rufe titunan sai dai kawo yanzu ba'a kama kowa ba. (Ahmad)