Hedkwatar rundunar 'yan sandan birnin London, ya ce an kama mutane 12 wadanda ke da alaka da harin da aka kai birnin a ranar Asabar da dare, yayin samamen da aka kai gidan daya daga cikin maharan a yankin Barking dake gabashin birnin London.
Har ila yau, rundunar ta ce jami'an tsaro na ci gaba da binciken wasu gidaje a yankin na Barking.
Kafar yada labarai ta Sky News ta ruwaito mutanen dake zaune a rukunin gidaje na Elizabeth Fry dake titin Kings na Barking, inda gidan daya daga cikin maharan yake na cewa, an yi ta harbe-harbe kuma jami'an tsaro dauke da manyan makamai ne suka kai samame da sanyin safiyar jiya. (Fa'iza Mustapha)