Guterres ya yi kiran da a hanzarta gurfanar da wadanda suka aikata wannan ta'asa a gaban kotu. Sa'an nan ya mika sakon ta'aziya ga gwamnati da al'ummar Najeriya da ma iyalan wadanda suka rasa rayukansu sakamakon harin, tare da fatan wadanda suka jikkata za su samu sauki cikin hanzari. (Bello Wang)