in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar nazarin Sin ta kaddamar da sabon rahoto game da ci gaban Afirka
2018-08-14 20:24:12 cri
A kwanan baya ne sashen nazarin harkokin yammacin Asiya da Afirka na kwalejin nazarin kimiyyar zaman takewar al'ummar kasar Sin ya kaddamar da wani rahoto game da ci gaban Afirka tsakanin shekarar 2017 zuwa 2018, inda aka nazarci sabon yanayin da nahiyar Afirka ke ciki a fannonin siyasa, tattalin arziki, tsaro, alaka da ketare, dokoki da kuma kafofin watsa labaru.

Baya ga haka, rahoton ya kuma nuna cewa, dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka na da kyau kamar yadda kafofin watsa labarun nahiyar Afirka ke kallo, kana yawan jarin da Sin ke zubawa a Afirka na karuwa. Rahoton ya ce, akwai tunanin bangarorin biyu za su karfafa hadin kai wajen yin cudanya a fannonin siyasa, manyan ayyuka, cinikayya, harkokin kudi da kuma kara fahimtar juna a tsakanin al'ummunsu da dai sauransu. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China