in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An ceto bakin haure 27 a gabar tekun yammacin Libya
2018-08-03 09:30:03 cri
Jami'an tsaron tekun birnin Zuwara na yammacin kasar Libya, mai tazarar kilomita 120 daga yammacin Tripoli babban birnin kasar, a jiya Alhamis sun yi nasarar ceto bakin haure ta haramtacciyar hanya kimanin 27, wadanda suka hada da mata a lokacin da suke fuskantar barazanar nitsewa a tekun a kan hanyarsu ta tsallakawa kasashen turai.

Tawagar jami'an tsaron tekun masu yaki da bakin haure na birnin Zuwara sun yi nasarar ceto bakin hauren su 27 ne daidai lokacin da suke daf da rasa rayukansu kamar yadda sashen hukumar tsaron na Zuwara ya sanar.

Sanarwar ta ce, bakin hauren da aka ceto sun fito ne daga kasashe da dama daga Afrika da kasashen larabawa, daga cikinsu akwai mata 5 da wata karamar yarinya.

Tuni dai aka samar da tallafin magunguna ga 'yan ciranin, kana hukumomin tsaro na cigaba da bincike a birnin don gano musabbabin da ya haddasa hadarin.

A ranar Laraba, sojojin ruwan kasar Libya sun sanar da cewa sun ceto 'yan cirani kimanin 574 a gabar tekun yammacin kasar a aikin sintirin da suka gudanar sau uku a jere. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China