in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban majalisar zartarwar Libya ya yi murabus
2018-07-19 10:50:57 cri
Mataimakin shugaban majalisar zartarwa ta kasar Libya da MDD ke marawa baya, wato Fathi al-Majbari, ya yi murabus jiya da yamma.

Gidan talabijin na al-Hadath na kasar, ya ruwaito Fathi al-Majbari ya na sanar da yin murabus daga mukaminsa da kuma Gwamnatin hadin kan kasar, tare da yin kira ga dukkan ministocin da ke kishin kasar su ma su ajiye mukamansu.

Ya ce Tripoli na karkashin ikon 'yan tawaye, kuma sun yi kokarin gyara hakan amman sun gaza, yana mai cewa ba birni ne da ya dace da tsarin siyasa ba, sannan ya na bukatar kulawa sosai.

Ya kara da cewa, gwamnati ta gaza samar da tsaro ga al'ummarta.

Har ila yau, ya ce 'yan tawayen ne ke iko da harkokin kudi, kuma abun dake gudana cikin gwamnatin hadin kan kasar, wasa ne kawai. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China