in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya halarci taron tattaunawa tsakanin shugabannin kasashen BRICS da na wasu kasashe masu tasowa
2018-07-27 21:33:03 cri

Yau Juma'a aka shirya taron tattaunawa tsakanin shugabannin kasashen BRICS da na wasu kasuwanni da kasashe masu tasowa a birnin Johanneburg na kasar Afirka ta kudu, inda shugabanni mahalartan taron suka tattauna kan manyan manufofin da suka shafi hadin kan kasa da kasa a fannin ci gaba, da na hadin kai tsakanin kasashe masu tasowa, sun kuma kai ga cimma ra'ayin bai daya. Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci taron tare kuma da gabatar da jawabi.

A yayin jawabinsa, shugaba Xi ya nuna cewa, yanzu ana cikin wani lokaci na neman babban ci gaba da samun manyan sauye-sauye, hakan ya sa kasuwanni masu tasowa da kasashe masu tasowa, ke fuskantar dama da kalubale na bai daya. Don haka, yana da muhimmanci a karfafa hadin kai a tsakaninsu.

Shugabannin kasashen BRICS, da shugabanni ko wakilansu, na wasu kasashen da aka gayyata, sun hada da na Angola, Argentina, jamhuriyar demokuradiyyar Kongo, Garbon, Malawi, Senegal, Togo da dai sauransu, da kuma wasu jami'an kungiyoyin nahiyar Afirka. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China