in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi ya yi kira ga kasashe mambobin BRICS su yi aiki domin kyautata sabuwar alakar kasa da kasa
2018-07-26 21:43:39 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira ga kasashe mambobin kungiyar BRICS, da su yi aiki tare, domin kyautata sabuwar alakar kasa da kasa mai kunshe da martaba juna, da daidaito, da adalci, wanda kuma zai haifar da cimma moriyar juna.

Shugaba Xi wanda ya bayyana hakan a Alhamis din nan, yayin taron kolin kungiyar BRICS karo na 10 dake gudana a birnin Johannesburg, na Afirka ta kudu, ya ce "ta amfani da rawar da taron ministocin wajen kasashe mambobin BRICS ka iya takawa, da mashawarta a fannin tsaro, da kuma wakilan dindindin na MDD, za mu iya bayyana muryar mu, tare da gabatar da hanyar mu ta warware matsaloli".

Taron kungiyar BRICS na wannan karo dai ya tattara shugabannin kasashe da tattalin arzikinsu ke samun saurin ci gaba, da suka hada da Brazil, da Rasha, da India, da Sin da kuma Afirka ta kudu.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China