in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 2 sun mutu sanadiyyar raunukan da suka ji biyo bayan fashewar wani abu yayin gangamin zabe a Zimbabwe
2018-06-26 10:09:49 cri

Mutane biyu da suka jikkata ranar Asabar da ta gabata sanadiyyar fashewar wani abu a wajen gangamin zabe a Bulawayo na Zimbabwe, sun mutu.

Karamar Minista mai kula da yankin Bulawayo Angeline Masuku, da ta tabbatar da mutuwar a jiya, ta ce mutanen biyu sun mutu ne sanadiyyar fashewar wani abu jim kadan bayan Shugaban kasar Emmerson Mnangagwa ya kammala jawabi ga gangamin.

Shugaba Mnangagwa ya tsira ba tare da kwarzane ba, duk da cewa mataimakinsa Kembo Mohadi da wasu 48 sun samu raunuka.

Tuni Mnangagwa ya bayyana harin a matsayin na tsoro daga makiyayansa, inda ya lashi takobin za a gudanar da babban zaben kasar a ranar 30 ga watan Yulin kamar yadda aka shirya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China