in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kafofin watsa labaru na Afirka suna son kara hadin gwiwa tare da kafofin watsa labaru na kasashen BRICS
2018-07-20 15:00:23 cri
Wakilan kafofin watsa labaru na Afirka, sun bayyana a gun dandalin tattaunawa, na kafofin watsa labarun kasashen BRICS karo na 3 da aka gudanar a birnin Cape Town a ranar 19 ga wata cewa, suna son kara yin hadin gwiwa, tare da kafofin watsa labaru na kasashen BRICS, da gabatar da labarai game da hakikanin Afirka.

Wakilin mujallar "Exchange" ta kasar Tanzania Aly Ramji ya bayyana cewa, hukumomin kafofin watsa labaru na kasashen BRICS, sun iya taimakawa kafofin watsa labaru na Afirka wajen raya karfinsu, don gabatar da labarai ta hanyar idon Afirka.

Wakilin kamfanin watsa labaru na "New Times" na kasar Ghana Carol Annang ya bayyana cewa, ya kamata kafofin watsa labaru na Afirka su yi hadin gwiwa tare da na kasashen BRICS, da kara fahimtar juna da yin imani da juna don kafa dandalin watsa labaru na Afirka, da kaucewa daga tsarin sarrafawa na hukumomin wasu kasashen yammacin duniya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China