in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani jami'in kasar Afirka ta kudu ya jinjinawa nasarorin da kungiyar BRICS ta cimma a shekaru 10
2018-07-20 13:51:00 cri
Darakta mai kula da sashen cinikayya da raya masana'antu a Afirka ta kudu Lerato Mataboge, ya jinjinawa nasarorin da kungiyar BRICS ta cimma a cikin shekaru 10 da suka gabata, yana mai cewa kungiyar na iya cimma karin nasarorin masu dama a nan gaba.

Mr. Mataboge ya bayyana kafuwar bankin samar da ci gaba na kungiyar ko NDB a takaice, a matsayin daya daga cikin manyan nasarorin da kungiyar ta cimma.

Jami'in wanda ke jawabi yayin wani zaman tattaunawa na masu ruwa da tsaki, game da ayyukan kungiyar da ya gudana a jiya Alhamis ya kara da cewa, Afirka ta kudu ta ci gajiyar rance daga bankin wanda ke samar da isassun kudade na gudanar da ayyukan more rayuwar jama'a. Kaza lika a cewar sa, kasar sa na fatan samun karin rance daga bankin a nan gaba.

A nasa tsokacin, wakilin Afirka ta kudun a kungiyar ta BRICS, ambasada Anil Sooklal, ya ce hadin gwiwar kasashe mambobin BRICS na ci gaba da fadada cikin sauri, inda baya ga hadin kai a fannin siyasa, yanzu haka kasashe mambobin kungiyar na zurfafa alakar su ta fannin musaya tsakanin al'ummun su, matakin da zai shafi daukacin sassa na inganta zamantakewar su. Mr. Sooklal ya kara da cewa, dukkanin kasashe mambobin kungiyar ta BRICS na adawa da duk wani nau'i na nuna wariya da kuma kulla yakin cinikayya. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China