in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babu wata kasa da ta fada rikicin basussuka sakamakon hadin gwiwa tare da kasar Sin
2018-07-16 19:46:11 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana cewa, sharhin da jaridar Financial Times ta kasar Birtaniya ta wallafa cewa wai aikin shawarar "ziri daya da hanya daya" yana fuskantar matsala a fadin duniya, wannan ra'ayi bai dace da yanayin da ake ciki ba, kuma Sin ta ki amince da shi.

Hua ta jaddada cewa, a cikin abokan hadin gwiwa na Sin, babu wata kasa da ta fuskanci rikicin basussuka sakamakon hadin gwiwa tare da kasar Sin. Rikicin basussukan da ya faru da ake magana a kai ba shi da nasaba da kasar Sin.

Hua Chunying ta bayyana cewa, wasu kasashe masu tasowa suna fuskantar matsin lamba kan tattalin arzikinsu, kana an samu juyin juya hali da fuskantar bala'u a wasu kasashe, wasu matsaloli da aka fuskanta na dan wani lokaci a aikin "ziri daya da hanya daya" matsala ce da aka saba fuskanta yayin da ake kokarin samun bunkasuwa, kuma tilas a warware su ta hanyar yin shawarwari a tsakanin bangarorin da abin ya shafa. Sin tana fatan kafofin watsa labaru za su rika bayar da labaran gaskiya cikin adalci bisa hakikanin halin da ake ciki daga dukkan fannoni. (Zainab Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China