in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude taron ministoci na dandalin hadin gwiwar kasar Sin da kasashen Larabawa
2018-07-10 10:57:30 cri
A yau ne aka yi bikin bude taron ministoci karo na 8 na dandadin hadin gwiwar kasar Sin da kasashen Larabawa a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin. Shugaban kasar Sin Xi Jinping, da Sarkin Musulmi na kasar Kuwait Sheikh Al-Sabah, da babban sakataren kungiyar kawancen kasashen Larabawa Ahmed Aboul-Gheit, gami da ministoci na wasu kasashen Larabawa 21 sun halarci bikin budewar, inda shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya yi jawabi don bayyana manufofin kasar Sin ta fuskar hadin gwiwa da kasashen Larabawa.

Cikin jawabinsa, shugaba Xi ya ambaci yadda za a kara kyautata huldar dake tsakanin Sin da kasashen Larabawa, da tsare-tsare masu alaka da hadin gwiwarsu, da matakan da za a dauka don kyautata fasalin dandalin hadin gwiwar. Ban da haka kuma, shugaban ya bada shawarwari game da yadda kasar Sin da kasashen Larabawa za su kara hada kai wajen aiwatar da shawarar "Ziri daya da Hanya daya", gami da bayyana shawarar kasar Sin kan wasu matsalolin da ake fuskanta a yankin gabas ta tsakiya, don neman biyan bukatun bangarori daban daban masu ruwa da tsaki. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China