in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afrika ta karrama tsohon jami'in MDD mai kula da nahiyar Afrika
2018-07-08 15:37:53 cri
Nahiyar Afrika ta gudanar da bikin karrama marigayi Adebayo Adedeji, wanda ya rike mukamin babban sakataren hukumar kula da tattalin arzikin Afrika na MDD wato (ECA), wanda ya jagoranci hukumar sama cikin shekaru 16.

Nahiyar, karkashin shugabancin hukumar ta ECA, ta samu gagarumin ci gaba bisa gudunmowa da kuma irin jajurcewar da marigayi Adedeji ya nuna ta hanyar shirya taruka da tattaunawar da ya jagoranta lokacin ya rike da ragamar shugabancin hukumar, an yi bikin binne shi a ranar Juma'a a kasarsa ta haihuwa Najeriya.

Daruruwan shugabannin tsare tsare na Afrika da kwararru cikinsu har da shugabannin wasu kasashen Afrika da suka hada da shugaban kasar Namibia Hage Geingob, da mataimakin shugaban Najeriya Yemi Osinbajo, da tsahon shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo, da kuma manyan jami'an hukumar ECA ne suka bayyana jinjinarsu bisa ga irin nasarorin da Adedeji ya samar ga ci gaban Afrika, kamar yadda hukumar MDDr ta sanar a jiya Asabar.

Adedeji, wanda ya shugabanci hukumar ECA na tsawon shekaru 16 daga shekarar 1975 zuwa 1991, an bayyana jami'in a matsayin wani babban jigo kuma jagoran tabbatar da cigaban nahiyar Afrika a karni na 20. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China