in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sifeton 'yan sandan Najeriya ya bukaci yin hadin gwiwa don kawar da muggan laifuka a kasar
2018-07-06 09:18:42 cri
Babban sifeton 'yan sandan Najeriya Ibrahim Idris ya bukaci al'ummomin yankunan kasar da su hada gwiwa da jami'an 'yan sanda domin yaki da ayyukan bata gari a duk fadin kasar.

Da yake jawabi a taron koli game da al'amurran tsaro a jahar Imo dake kudancin kasar, Idris ya ce kamata ya yi al'ummomin yankunan kasar su hada kai da jami'an 'pyan sandan wajen gano bata gari domin dakile ayyukan bata garin.

Ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa tsakanin al'ummomi da 'yan sanda, ya ce jami'an 'yan sandan ba za su iya kawo karshen matsalolin tsaro dake zama barazana a kasar ba tare da samun goyon bayan jama'a ba.

Idris ya fadawa mahalarta taron cewa, 'yan sanda suna bukatar hanyoyin sadarwa, da fasahohin sadarwa na zamani, da na'urorin gudanar da bincike na zamani wadanda za su taimaka musu wajen gudanar da ayyukan bincike.

Sifeton ya bukaci 'yan kasar da su yabawa kokarin da jami'an 'yan sandan kasar ke yi bisa irin nasarorin da suka cimma kawo yanzu game da yaki da bata gari a fadin kasar.

Jami'in ya buga misali da irin nasarorin da 'yan sandan Najeriyar suka samu na baya bayan nan musamman a yankin kudu maso gabashin kasar wadanda suka hada da damke shahararren mai yin garkuwar da mutanen nan da aka fi sani da Vampire da kuma kama wani shahararen mai garkuwa da mutanen mai suna Evans. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China