in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na fatan taron ministoci da za a yi zai aike da bayanannen sako game da ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar nukiliyar Iran
2018-07-06 10:00:15 cri
Dan majalisar gudanarwar kasar Sin kuma Ministan harkokin wajenta, Wang Yi, ya bayyana yakinin ganin taron dake karatowa, na ministocin harkokin wajen kasashen dake cikin yarjejeniyar nukiliyar Iran, zai aike da bayanannen sakon hadin kai, game da ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar nukiliyar.

Wang Yi ya bayyana haka ne lokacin da yake amsa tambayoyi, yayin wani taron manema labarai na hadin gwiwa da ya yi da takwaransa na Austria, Karin Knessl.

Taron wanda zai gudana yau Juma'a a Vienna, da zai kunshi Ministocin harkokin wajen Faransa da Jamus da Rasha da Birtaniya da Iran da Columbia da Sin, shi ne irinsa na farko da za a yi tsakanin bangarorin da suka rage cikin yarjejeniyar Nukiliya Iran, tun bayan janyewar Amurka.

A cewar Wang Yi, gazawa wajen ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar, ba batun Nukiliya Iran kadai za ta yi wa illa ba, ya na mai cewa, za ta yi mummunan tasiri kan lokacin da ake ciki na son kawar da makaman nukiliya da kuma yanayin yankin gabas ta tsakiya.

Ministan da ya bayyana taron na yau a matsayin wanda ake bukata kuma ya zo a kan gaba, ya ce a shirye kasar Sin ta ke ta yi aiki da bangaren Turai, wajen ci gaba da yin dukkan mai yiwuwa don ganin an aiwatar da yarjejeniyar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China