in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta ce sabuwar yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Sudan ta Kudu za ta gaggauta ayyukan jin kai
2018-06-30 15:42:32 cri
Shirin wanzar da zaman lafiya na MDD dake aiki a Sudan ta Kudu UNMISS, ya ce sabuwar yarjejniyar tsagaita bude wuta ta dindin-din da aka cimma a Sudan ta Kudu, za ta taimaka wajen gaggauta kai kayakin agaji ga yankunan kasar dake da bukata.

Wakilin Sakatare Janar na MDD kuma shugaban shirin UNMISS David Shearer, ya ce yarjejeniyar da aka cimma a Khartoum ranar Laraba da ta gabata, ya bude wani sabon babi kuma ya karfafawa shirin gwiwa.

David Shearer ya shaidawa manema labarai a birnin Juba cewa, a ganinsa, yarjejeniyar wani yunkuri ne na ci gaba, sannan mafari ne na samar da cikakkiyar yarjejeniyar zaman lafiya mai dorewa, wadda za a tattauna kanta cikin makonni masu zuwa.

Ya kuma yi kira ga bangarorin dake fada da juna, su sake shiga yarjejeniyar, ya na mai cewa babu yadda za a yi a wanzar da zaman lafiya a lokacin da ake tsaka da rikici a kasa.

Ya kara da cewa, idan bangarori masu fada za su kara kokari akan yarjejeniyar tsagaita bude wutan domin tabbatar da ya yi aiki, to akwai dama da masu ruwa da tsaki ke ganin za a zauna don nazarin sauran batutuwa. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China