in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakataren MDD ya yabawa kokarin IGAD na samar da zaman lafiya a Sudan ta kudu
2018-06-28 09:51:07 cri
Babban sakataren MDD Antonoi Guterres ya yabawa rawar da kungiyar raya kasashen gabashin Afirka ta IGAD ke takawa game da farfado da dandalin da zai jagoranci shirin wanzar da zaman lafiya a Sudan ta kudu.

Jami'in na MDD wanda ya bayyana hakan ta hannun kakakinsa Stephane Dujarric, ya ce ya gamsu da aniyar bangarorin da abin ya shafa na ci gaba da sasantawa. A don haka ya bukaci dukkan bangarorin da abin ya shafa da su nuna halin ya kamata na ganin sun kai ga cimma yarjejeniya a kan batutuwan da ba a kai ga cimmawa ba a fannonin shugabanci da ma matakan tsaro.

Ya ce, a shirye MDD da kungiyoyin IGAD da AU suke na goyon bayan gwamnati da al'ummar Sudan ta kudu, wajen ganin an aiwatar da yarjejeniyar da kowa ne bangaren zai yin na'am da ita.

Tun a ranar Larabar da ta gabata ce dai shugaban Sudan ta kudu Salva Kiir da jagoran 'yan adawar kasar Riek Machar suka amince da tsagaita bude wuta na din-din-din, wadda za ta fara cikin sa'o'i 72, lamarin da ake fatan zai kawo karshen rikicin shekaru da rabi da ya addabi kasar.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China