in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakataren MDD ya yi Allah wadai da kisan ma'aikatacin wanzar da zaman lafiya a Sudan ta kudu
2018-06-27 11:29:41 cri
Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya yi Allah wadai da kisan ma'aikacin dake akin wanzar da zaman lafiya a Sudan ta kudu.

Guterres wanda ya bayyana cikin wata sanarwa ta hannun kakakinsa Stepahane Dujarric, ya kuma mika sakon ta'aziyya ga gwamnatin Bangaladesh da iyalan wadanda harin ya rutsa da shi.

Jami'in na MDD ya sake nanata cewa, kaiwa ma'aikatan wanzar da zaman lafiya na MDD hari na iya zama laifi na yaki. Ya kuma nanata goyon bayansa ga ma'aikata maza da mata dake aiki karkashin laimar MDD a kasar Sudan ta kudu, a kokarin da suke yi na kare rayukan fararen hula da ma tabbatar da zaman lafiya a kasar da yaki ya wargaza.

A jiya ne dai aka halaka wani ma'aikacin wanzar da zaman lafiya na MDD dan kasar Bangaladesh a wani harin da aka kaiwa tawagar su da ke samar da kariya ga ma'aikatan bayar da agajin jin kai ga al'ummomin dake tsakiyar yankin Equatoria na kasar Sudan ta kudu. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China