in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
SACU ta bayyana tabbaci kan farfadowar tattalin arziki
2018-06-28 10:19:46 cri
Kungiyar hukumomin kwastan na kasashen kudancin Afirka( SACU) tana da tabbacin cewa, tattalin arzikin kasashen nahiyar zai farfado, biyo bayan farfadowar farashin kayayyaki da yadda tattalin arzikin kasashen da suka ci gaba da ma wadanda ke tasowa ke ci gaba da bunkasa.

Ministan kudi da raya tattalin arziki na kasar Bostswana Kenneth Matambo Minista shi ne ya bayyana hakan yayin bude taron majalisar ministocin kungiyar SACU karo na 35 da ya gudana jiya a Gaborone, fadar mulkin kasar Botswana. Ya ce kasashen dake kungiyar sun yi hasashen samun matsakaicin ci gaba, ganin tarin damammakin da suka karade duniya wadanda ci gaban tattalin arziki duniya ya kawo.

Ya ce, yayin da kasashe mambobin SACU ke da tabbaci game da makomar ci gaban duniya, suna kuma nuna damuwa game da yadda ake ba da kariya ga harkokin cinikayya da karuwar cacar-bakin cinikayya tsakanin Amurka a hannu guda da kuma abokan cinikayyarta a daya bangaren.

A don haka Matambo ya ce, akwai bukatar tattaunawa tsakanin kasashe, don cimma daidaito ta yadda za a warware wadanan matsaloli.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China