in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Algeria ta ce a shirye take ta yi musayar gogewarta a fannin yaki da ta'addanci
2018-06-25 10:20:35 cri
Ministan harkokin wajen Algeria Abdelkader Messahel, ya jadadda cewa, a shirye kasarsa ta ke ta yi musayar gogewar da take da shi ta fuskar yaki da kaifin kishin addini da ta'addanci.

Abdelkader Messahel ya bayyana haka ne yayin bude wani taron yanki karo na 3, kan kare kaifin kishin addini da ya gudana a Algiers, babban birnin kasar.

Ya kuma ce manufar taron ita ce, musayar kyawawan ayyuka da gogewa, wanda Algeria ke da su a matakai daban-daban.

Ministan ya ce babbar manufar irin taron ita ce, tattara kokarin kasashe daban-daban tare da karfafa kwarewarsu na yaki da barzanar da bata da iyaka.

Har ila yau, ya ce kafofin sadarwa na zamani da rashin kudi tsakanin matasa ne ke taimakawa yaduwar tsattsauran ra'ayi da kaifin kishin addini a wasu sassan Afrika. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China