in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta ce Amurta tana yunkurin saba yarjejeniyar ciniki da bangarorin biyu suka cimma
2018-05-30 09:24:33 cri
Ma'aikatar cinikin kasar Sin (MOC) ta sanar a jiya Talata cewa, kalaman Amurka ya ci karo da yarjejeniyar ciniki da bangarorin biyu suka cimma a kwanakin baya a birnin Washington.

Ma'aikatar cinikin ta ce, kalaman na White House wasu irin bayanai ne wadanda bai kamata bangarorin biyu su tsammaci hakan ba, bisa abin da ake sa ran faruwarsa game da wannan batu.

MOC ta sanar a shafinta na intanet cewa, "Ko ma wanne irin mataki Amurka za ta dauka, kasar Sin tana da kwarin gwiwa, kuma tana da karfin iko da kwarewar da zata kare muradun al'ummarta da kuma moriyar kasarta".

Sanarwar ma'aikatar cinikin ta ce, kasar Sin ta bukaci Amurka da ta zartar da abin da ya dace karkashin yarjejeniyar da bangarorin biyu suka cimma a kwanan nan. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China