in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilan jami'yyun siyasu sun yaba manufar kasar Sin na yin gyare-gyare da bude kofa ga ketare
2018-05-28 10:42:12 cri
Mahalarta taron jam'iyyun siyasu da ya gudana a birnin Shenzen dake kudancin kasar Sin sun bayyana cewa, manufar kasar Sin ta yin gyare-gyare da bude kofa ga kasashen waje ta haifar da gagarumin sakamako da kyakkyawan darasi ga duniya baki daya.

A jawabinsa kwamitin lardin Guangdong na JKS Li Xi ya ce taron na wannan shekara, ya zo daidai da cika shekaru 40 da fara aiwatar da manufar kasar Sin ta zurfafa yin gyare-gyare da bude kofarta ga kasashen waje. Kuma birnin Shenzhen na lardin Guangdong, a nan ne aka fara aiwatar da wannan manufa. Daya daga cikin nasarorin da aka cimma karkashin wannan manufa shi ne yankin tattalin arziki na musamman dake Shenzhen.

"Shenzhen dai dan karamin gari ne da ya shahara a fannin kamun kifi. Amma daga bisani, garin ya gawurta, kuma yanzu haka akwai kimanin gine-gine 1,000 masu tsayin sama da mita 100. " In ji tsohon shugaban kwamitin harkokin waje na majalisar dattawan kasar Pakistan Mushahid Hussain Syed wanda ya taba ziyarar birnin Shenzhen a matsayin dan jarida shekaru 40 da suka gabata. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China